Shugaban Ecowas, Bola Tinubu, ya umarci Babban Bankin Najeriya ya sanya Æarin takunkuman kuÉi a kan hukumomi da ÉaiÉaikun mutanen da ke da alaÆa da shugabannin juyin mulki a Nijar.
Wata sanarwa da mai bai wa shugaban na Najeriya shawara na musamman kan harkar yaÉa labarai, Anjuri Ngalale ta ce Tinubu ya umarci gwamnan babban bankin na CBN ya ÆaÆaba wasu jerin takunkumai a kan masu hulÉa da sojojin da ke mulkin Nijar.
Matakin na zuwa bayan Æarewar wa’adin mako Éaya da Æungiyar Ecowas ta bai wa sojojin Nijar bisa tanadin yarjejeniyar sanya takunkuman kuÉi na shugabannin Æasashen Æungiyar Ecowas.
Shugaba Tinubu ya ce bai Éauki matakin cikin kuskure ba ne, saboda ya samu izini daga takwarorinsa na Ecowas don fitar da sanarwa, ya kuma nanata cewa matsayin, ba al’amari ne da ya Éauka da sunan wani shugaban Æasa guda Éaya ba.
Ya ce takunkuman da aka sanya wa Nijar, mataki ne da ya Éauka a matsayinsa na shugaban Ecowas, kuma shugaban Najeriya, amma yana tsaye a kan ikon da yarjejeniyar Æudurin dukkan Æasashe wakilan Ecowas da shugabannin Æasashen Æungiyar.
A cewarsa, matakin iko ne, da ba na gwamnatin Najeriya ba, Æuduri ne da aka zartar a bainar jama’a kafin wannan lokaci. Shugaban Najeriyar dai yana mayar martani ne ga sukar da yake fuskanta a ciki da wajen Æasar game da matakin sanya wa Nijar takunkumai da barazanar Éaukar matakin soji na Æungiyar Ecowas, bayan hamÉarar da Shugaba Mohamed Bazoum daga mulki.
Tinubu ya ce bayar da wa’adi ga Nijar, hurumin Ecowas ne, ba na Najeriya ba.
A cewarsa Najeriya, ba ta bai wa Nijar wani wa’adi ba. Sanarwar ta kuma ambato shugaban Najeriyar na cewa a ‘yan kwanakin nan, bayan cikar wa’adin Ecowas, ya faÉada tuntuÉa a ciki da wajen Æasar ciki har da musayar ra’ayi da gwamnonin jihohi masu iyaka da Nijar dangane da abin da ya faru a maÆwabciyar Æasar.
Amma Shugaba Tinubu ya nanata Æudurin cewa duk martanin da Ecowas ta mayar da kuma wanda za ta mayar a kan batun juyin mulkin Nijar, zai kasance ne ba tare da la’akari ko tunanin bambancin Æabila ko addini ba.y
Ya ce Æungiyar ta Æunshi dukkan Æabilu da addinai daban-daban da kuma sauran nau’o’in bambance-bambancen al’ummomin Afirka ta Yamma, don haka martanin Ecowas zai kasance ya yi la’akari da duk waÉannan Éangarori, amma ba wani daga cikinsu ba.
Ya ce duk da yake babu wani zaÉi da aka Éauke a jerin matakan da za a iya amfani da su, Æungiyar za ta gudanar da taron Æoli a Abuja ranar Alhamis, inda ake sa rai Ecowas za ta cimma muhimman shawarwari a kan matakai na gaba a kan Nijar.
BBC Hausa
Discover more from Albarka Radio
Subscribe to get the latest posts sent to your email.








