Skip to content
September 14, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Mutum 76 sun shiga hannun jami’an tsaro bisa yunkurin auren jinsi a Gombe

October 23, 2023 1 minute read

Rundunar tsaro ta Civil Defence Corp a Nijeriya ta ce ta kama akalla mutum 76 da ake zargi da yunkurin yin auren jinsi a Jihar Gombe da ke arewa maso gabashin kasar.

Mai magana da yawun rundunar reshen Jihar Gombe SC Buhari Sa’ad ne ya bayyana haka a ranar Lahadi inda ya ce sun samu nasarar kama matasan ne bayan sun samu bayanan sirri cewa suna shirin wani biki na zagayowar ranar haihuwa da kuma auren jinsi.

Sa’ad ya shaida wa manema labarai cewa cikin mutu 76 da ake zargi, 59 maza ne inda 21 daga cikinsu suka tabbatar da cewa su ‘yan luwadi ne sai kuma akwai mata 17 wadanda aka kama a wurin.

Ya ce da zarar an kammala bincike za a gurfanar da waɗanda ake zargi a gaban kotu.

Ba wannan ne karon farko da ake kama masu auren jinsi ba a Nijeriya domin ko a watan Yulin bana sai da hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama wasu da ake zargi da auren jinsi.

Haka ma a watan Agustan da ya gabata rundunar ‘yan sandan Jihar Delta ta kama sama da mutum 100 wadanda ake zarginsu da auren jinsi.

TRT Afrika Hausa

Tags: Auren jinsi Gombe Luwadi NSCDC

Post navigation

Previous: Malamin islamiyya ya ce ga garinku bayan shan duka a wajen surukansa a Neja
Next: Saurayi Da Budurwa Sun Daurawa Kansu Aure A Jigawa

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.