Kungiyar Lauyoyi ta Kasa (NBA) reshen Jihar Gombe ta lashi takobin ganin an hukunta wasu wadanda suka kai wa alkalin babbar kotun jihar tare da maâaikatansa hari suka sassare su.
Shugaban kungiyar a jihar, Barista Benjamin Sati, ya ce muddin irin haka na faruwa da akalai da maâaikatan kotu, to kasar nan babu wanda zai tsira.
Sanarwar da ya fitar bayan zuwa biyar alkalin da maâaikatan nasa da aka yi wa duka aka sassare shi, ta nuna rashin jin dadinsu kan wadanda suka yi masa wannan danyen aiki.
âUsman Yahaya, wanda ya ji mummunan rauni yana samun sauki, muna kira ga mambobin kungiyarmu da kada su fusata, su bai wa shugabani hadin kai wajen bin lamarin a hankali don cimma nasara,â in ji Sati.
Ya bukaci hadin kan dan sanda mai bincike na ofishin âyan sanda da ke garin Talasse wanda zai sanar da ofishin kwamishinan âyan sanda abin da ya faru ta hannun babban jamiâi mai kula da sashen shariâa wanda yana cikin tawagar da suka kai ziyarar.
Jaridar Aminiya
Discover more from Albarka Radio
Subscribe to get the latest posts sent to your email.









