Home Labarai Ƴan Najeriya za su iya zuwa Dubai Yanzu

Ƴan Najeriya za su iya zuwa Dubai Yanzu

 

HaÉ—aÉ—É—iyar Daular Larabawa ta cire haramcin biza a kan ‘yan Najeriya, kamar fadar shugaban Najeriya ta bayyana.

Wata sanarwa daga fadar shugaban ta United Arab Emirates (UAE) ta É—auki matakin ne bayan ganawar da Shugaba Bola Tinubu ya yi da takwaransa Mohamed bin Zayed Al Nahyan a yau Litinin a birnin Abu Dhabi.

“Kazalika, wannan yarjejeniyar na nufin kamfanonin zirga-zirgar jiragen sama na Etihad da Emirates za su ci gaba da shiga da fita a Najeriya nan take,” in ji sanarwar da Ajuri Ngelale ya fitar.

Ta ƙara da cewa yarjejeniyar ba ta ƙunshi biyan wani kuɗi ba a nan kusa tsakanin ƙasashen, yana mai nuni da miliyoyin dalolin da gwamnatin Najeriya ta riƙe wa kamfanonin jiragen na kuɗin tikiti.

Kusan shekara É—aya ke nan da UAE ta dakatar da bai wa matafiya daga Najeriya biza, a rikicin da ya samo asali tun daga lokacin annobar korona.

BBC Hausa


Discover more from Albarka Radio

Subscribe to get the latest posts sent to your email.