Wasu da ake zargin âYan Kalare ne sun yi wa wata mata mai âyaâya takwas yankan rago a garin Gombe.
Maharan sun shiga gidan Malama Aishatu Abdullahi mai shekaru 58 ne a daren Jumaâa, suka yi mata yankan rago a unguwar Jekadafari
Wani rahoto da Aminiya ta samu daga hadimin Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya kan shaâanin tsaro da harkokin gwamnati, Ambasada Yusuf Musa Danbayo, ya ce ana kyautata tsamnanin turo su aka yi su kashe matar.
Ya bayyana cewa maharan sun shiga gidan Malama Aishatu ne da misalin karfe 9 na dare aka yi mata yankan rago sannan suka tsere da wayar salularta.
Hadimin gwamnan ya ce bayan faruwar lamarin an sanar da âyan sanda kuma nan take suka ziyarci gidan suka dauke ta zuwa asibitin kwararru na jihar.
Kakakin âan sandna jihar, ASP Mahid Muâazu Abubakar, ya ce a lokacin da âyan sandan suka isa gidan marigayiywar sun tarar da ita kwance male-male cikin jini, suka dauke ta zuwa asibitin inda a nan ne likita ya tabbatar da mutuwar ta.
Jamiâin ya ce, kwamishinan âYan Sanda Mai Kula da Ayyukan, Hayatu Usman a madadin kwamishinan âyan sandan jihar, ya ba da umarnin a gagguata fara bincike don gano wadanda suka aikata wannan danyen aiki.
Ya kara da cewa rundunar ba za ta zauna ta nade hannu miyagun abubuwa irin haka na faruwa ba, don haka sai sun zakulo wadanda suka aikata laifin dan fuskantar shariâa.
Daga nan sai yace dokar nan da aka sanya ta takaita zirga- zirgar jamaâa daga karfe 12 na dare ta na nan ba canji.
Jaridar Aminiya
Discover more from Albarka Radio
Subscribe to get the latest posts sent to your email.









