Skip to content
September 14, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Anyi wa wata mata yankan rago a Gombe 

October 21, 2023 2 minutes read

 

Wasu da ake zargin ’Yan Kalare ne sun yi wa wata mata mai ’ya’ya takwas yankan rago a garin Gombe.

Maharan sun shiga gidan Malama Aishatu Abdullahi mai shekaru 58 ne a daren Juma’a, suka yi mata yankan rago a unguwar Jekadafari

Wani rahoto da Aminiya ta samu daga hadimin Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya kan sha’anin tsaro da harkokin gwamnati, Ambasada Yusuf Musa Danbayo, ya ce ana kyautata tsamnanin turo su aka yi su kashe matar.

Ya bayyana cewa maharan sun shiga gidan Malama Aishatu ne da misalin karfe 9 na dare aka yi mata yankan rago sannan suka tsere da wayar salularta.

Hadimin gwamnan ya ce bayan faruwar lamarin an sanar da ’yan sanda kuma nan take suka ziyarci gidan suka dauke ta zuwa asibitin kwararru na jihar.

Kakakin ’an sandna jihar, ASP Mahid Mu’azu Abubakar, ya ce a lokacin da ’yan sandan suka isa gidan marigayiywar sun tarar da ita kwance male-male cikin jini, suka dauke ta zuwa asibitin inda a nan ne likita ya tabbatar da mutuwar ta.

Jami’in ya ce, kwamishinan ’Yan Sanda Mai Kula da Ayyukan, Hayatu Usman a madadin kwamishinan ’yan sandan jihar, ya ba da umarnin a gagguata fara bincike don gano wadanda suka aikata wannan danyen aiki.

Ya kara da cewa rundunar ba za ta zauna ta nade hannu miyagun abubuwa irin haka na faruwa ba, don haka sai sun zakulo wadanda suka aikata laifin dan fuskantar shari’a.

Daga nan sai yace dokar nan da aka sanya ta takaita zirga- zirgar jama’a daga karfe 12 na dare ta na nan ba canji.

Jaridar Aminiya

Tags: 'Yan Sanda Gombe yan kalare Yankan rago

Post navigation

Previous: Majalisar wakilai ta nemi a kara albashin malaman Firamare zuwa N250,000, Sakandire N500,000, lakcarori N1m
Next: Malamin islamiyya ya ce ga garinku bayan shan duka a wajen surukansa a Neja

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.