Latest:
Labarai

Da Dumi-Dumi: Gwamnatin Sojin Nijar ta katse hulda da Najeriya

Gwamnatin sojin Nijar ta katse huldar diflomasiyya da Najeriya, Togo, Amurka da kuma ta fuskar tsaro da tsohuwar uwargijiyar kasarsu Faransa.

Gwamnatin sojin Nijar din ta kuma ki ganawa da wakilan da Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS), ta tura domin tattaunawa da ita.

Wani daga cikin wakilan ya shada da kamfanin dillancin labarai na AFP cewa kasa da awa 24 da isarsu birnin Yamai suka baro kasar Nijar, “ko kwana ba mu yi ba,” ballantana ganawa da Janar Abdourahamane Tiani kamar yadda aka tsara.

A ranar Laraba ne ECOWAS ta tura wakilan nata, karkashin jagorancin tsohon shugaban mulki sojin Najeriya, Janar Abdulsalami Abubakar, domin tattaunawa da gwamnatin sojin da ta yi wa Shugaba Mohamed Bazoum juyin mulki.

Da farko dai gwamnatin Najeriya ta sanar cewa kwamitin na Abdulsalami Abubakar zai gana da Janar Tiani inda zai  gabatar wa gwamnatin sojin da ta yi juyin mulki a Nijar bukatun ECOWAS.

Kungiyar wadda Shugaan Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu yake jagoranta, ta kakaba wa gwamnatin sojin ta Nijar takunkumin karya tattalin arziki, sannan a ranar Lahadi ta ba wa sojojin wa’adin mako guda su mika wa Bazoum mulkinsa.

Jaridar Aminiya

Leave a Reply