Dakarun sojojin Najeriya sun kashe mayaÆan Boko Haram biyu, a yankin Æaramar hukumar Konduga ta jihar Borno.
Kakakin rundunar, Birgediya-Janar Onyema Nwachukwu ya ce dakarun sun yi wa Æ´an Boko Haram Éin kwanton-Éauna ne a wata hanya da suka saba wucewa.
Nwachukwu, ya ce an yi musayar wuta tsakanin mayaÆan da dakarun soji, inda daga baya sojojin suka yi nasarar fatattakar su da kuma kashe biyu a ciki.
Haka kuma, kakakin rundunar sojin ya ce dakarun sun Æwato makamai iri daban-daban, da Æwaya da kuma kuÉi a hannun mayaÆan na Boko Haram.
Babban hafsan sojin Æasa na Najeriya Laftanar-Janar Taoreed Lagbaja, ya jinjina wa dakarun bisa ÆoÆarin su wajen kawar da abin da ya kira Éata-gari daga yankin arewa maso gabas da ma sauran sassan Najeriya.
BBC Hausa
Discover more from Albarka Radio
Subscribe to get the latest posts sent to your email.








