Latest:
Labarai

Sojojin Najeriya sun Kashe ƴan Boko Haram a Borno

Dakarun sojojin Najeriya sun kashe mayaƙan Boko Haram biyu, a yankin ƙaramar hukumar Konduga ta jihar Borno.

Kakakin rundunar, Birgediya-Janar Onyema Nwachukwu ya ce dakarun sun yi wa ƴan Boko Haram ɗin kwanton-ɓauna ne a wata hanya da suka saba wucewa.

Nwachukwu, ya ce an yi musayar wuta tsakanin mayaƙan da dakarun soji, inda daga baya sojojin suka yi nasarar fatattakar su da kuma kashe biyu a ciki.

Haka kuma, kakakin rundunar sojin ya ce dakarun sun ƙwato makamai iri daban-daban, da ƙwaya da kuma kuɗi a hannun mayaƙan na Boko Haram.

Babban hafsan sojin ƙasa na Najeriya Laftanar-Janar Taoreed Lagbaja, ya jinjina wa dakarun bisa ƙoƙarin su wajen kawar da abin da ya kira ɓata-gari daga yankin arewa maso gabas da ma sauran sassan Najeriya.

BBC Hausa

Leave a Reply