Ministar harkokin jin-Æai da kawar da talauci ta Najeriya, Betta Edu ta ce gwamnatin Æasar za ta yi aiki kafaÉa-da-kafaÉa da gwamnonin jihohi, da Æananan hukumomi da kuma shugabannin al’umma domin tantance cikakkun bayanan talakawan Æasar.
Misis Edu ta bayyana haka ne ranar Juma’a a lokacin hira da gidan talbijin na Channels.
Ta Æara da cewa gwamnati za ta yi hakan ne domin cimma burin ma’aikatar jin-Æai ta Æasar na fitar da miliyoyin ‘yan Æasar daga Æangin talauci.
”Abu na farko da za mu fara yi, shi ne tantance rajistar sunayen masu Æaramin Æarfi ta Æasar, domin tabbatar da cewa talakawan ne a cikinta, waÉanda suka cancanci shiga cikin rajistar,” in ji Ministar jin -Æayin.
Ta ci gaba da cewa a ‘yan makonnin baya-bayan nan an yi ta samun ce-ce-ku-ce daga Éangaren Æungiyar gamnonin Æasar da sauran Æungiyoyi, kan ingancin rajistar.
“Wasu na cewa ta yi, wasu kuma na cewa ba ta ba, saboda mutanen da ke cikinta, ba su ne suka cancanci shiga cikinta ba, an shigar da siyasa cikin wajen haÉa rajistar”, in ji ta.
BBC Hausa
Discover more from Albarka Radio
Subscribe to get the latest posts sent to your email.








