Latest:
Labarai

An Gurfanar Da Emefiele a gaban Kotu a Lagos

Dakataccen Gwamnan babban bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele, ya isa babbar kotun tarayya da ke Legas domin gurfanar da shi a gaban kotu bisa zargin mallakar makamai ba bisa ka’ida ba.

Jami’an hukumar tsaro na farin kaya (DSS) ne suka gurfanar da Emefiele a gaban kotu da misalin karfe 9:20 na safiyar ranar Talata.

Za a gurfanar da shi a gaban mai shari’a Nicholas Oweibo bisa tuhume-tuhume biyu na mallakar makamai da alburusai ba bisa ka’ida ba.

A ranar 13 ga watan Yulin 2023 ne, gwamnatin tarayya ta shigar da kara a gaban kotu kan tuhume-tuhume biyu da suka hada da safarar makamai da alburusai ba bisa ka’ida ba kan gwamnan CBN da aka dakatar.

Gwamnatin Tarayya ta zargi Emefiele da mallakar bindiga mai lamba JOJEFF MAGNUM 8371 ba tare da lasisi ba.

Leadership Hausa

Leave a Reply