Labarai

Shugaba Buhari Ya Umarci A Hukunta Sojan Da Ya Kashe Sheikh Goni Aisami

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi Allah-wadai da abin da ya kira “kisan babu gaira-babu-dalili da aka yi wa Sheikh Goni Aisami” wanda ake tuhumar wani sojan Najeriya da kashe shi bayan da shaihin malamin ya ya rage masa hanya a motarsa, kamar yadda ƴan sanda suka tabbatar.

Yayin da yake mayar da martani kan lamarin, cikin wata sanarwa da kakakinsa Mallam Garba Shehu ya fitar, Shugaban ya ce wannan mummunan kisan da sojan Najeriya yayi wa malamin da ya taimake shi ba hali ne da aka san sojojin kasar nan da shi ba, kuma ya yi hannun riga da horon da aka ba sojoji na nuna da’a da girmamawa da kare rayukan wadanda ba su aikata wani laifi ba.

Shugaba Buhari ya kara da cewa, a matsayi sa na babban kwamandan sojojin Najeriya, ya fusata matuka kan lamarin da jami’in tsaro da aka horas domin ya kare rayuka ya aikata.

Ya kuma yi kira ga hukumomin sojin kasar “da su hukunta wadanda suka aikata wannan kazamin laifin ba tare da bata lokaci ba, sannan su yi waje da ire-iren wadannan sojojin masu mummunan hali.”

A karshe ya mika sakon ta’aziyya ga gwamnatin Jihar Yobe da jama’ar jihar da kuma iyalan Sheikh Goni Aisami bisa wannan rashi.

Leave a Reply