Kungiyar tsofaffin daliban jami’i’on gwamnatin Najeriya, ta yi gargadin cewa yajin aikin da kungiyar malaman jami’a ta ASUU ke yi ka iya zama babban bala’i ga kasar.
A wata wasika da kungiyar ta fitar a ranar Litinin, ta yi kira ga gwamnati da ASUU su sake zama teburin sulhu domin magance matsalar.
Sama da watanni shida kenan da ASUU ta tsunduma yajin aiki a daukacin Najeriya, ko da yake wasu gwamnatocin jihohin Najeriya sun kira malamai su koma bakin aiki, idan ba haka ba babu mai biyansu albashi.
Malaman Jami’o’in na bukatar a kara musu albashi, da alawus-alawus da sauran bukatu.
Daya daga cikin abubuwan da ke kara tunzura yajin aikin shi ne, rashin biyan jami’o’i kudaden shiga da suka kai sama da Naira Tiriliyan 1.
Leave a Comment